Kungiyar ƙwadago ta NLC ta gudanar da zanga-zanga a faɗin Najeriya

Mambobin kungiyar kwadago ta NLC sun fara gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna adawarsu da cire tallafin man fetur.

A jihar Lagos masu zanga-zangar sun taru a karkashin gadar Ikeja inda suka fara zanga-zangar.

A can birnin tarayya Abuja an samu rahoton karya kofar shiga harabar majalisar tarayya a lokacin da aka yi kokarin hana yan kungiyar ta NLC shiga ciki.

A makon da ya gabata ne kungiyar ta NLC ta bawa gwamnatin tarayya wa’adin mako daƴa domin ta janye duk wasu tsare-tsarenta da ke musgunawa talaka.

Zanga-zangar dai ta gudana lafiya a jihohi da ke fadin Najeriya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]