Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda A Zamfara

Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai a hanyar Gusau zuwa Sokoto a karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara sun kashe ‘yan sanda hudu.

A cewar wani dan unguwar mai suna Haruna Musa, ‘yan bindigar sun yi wa jami’an ‘yan sandan kwantan bauna ne a kan hanya a ranar Litinin din da ta gabata.

Musa ya ce ‘yan bindigar sun bude wuta kan jami’an ‘yan sandan da ke wani shingen da suka kafa a wani wuri da ke kusa da garin Bungudu, inda suka kashe hudu daga cikinsu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]