Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Naɗa Masu Bada Shawara 20

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya naɗa masu bashi shawara su 20.

Shugaban majalisar, Ahmad Lawan shi ne ya gabatar bukatar shugaban ƙasar dake cikin wata wasikar da ya aikewa majalisar.

Bayan karanta wasikar, Sanata Ibrahim Gobir mai wakiltar mazabar Gabashin Sokoto ya bukaci majalisar da ta amince da bukatar shugaban ƙasar.

Kudirin na Gobir ya samu goyon bayan shugaban marasa rinjaye na majalisar Sanata Philip Aduda.

Majalisar Dattawan ta bawa kudirin kulawar gaggawa inda ta amince da bukatar nan take.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]