An ƙaddamar da matatar man Dangote

A yau Litinin ne matatar mai ta Dangote ta fara aiki.

An kera matatar man ne don fitar da ganga 650,000 a kowacce rana domin sarrafa ma’aunin danyen mai daga nahiyoyi uku na Afirka, Asiya da Amurka.

An kuma tattaro cewa matatar ta za ta kai rarar lita miliyan 38 na man fetur, dizal, kananzir da kuma man jiragen sama a kowace rana ga Najeriya.

Don haka za ta cika kaso 100 na man da kasar ke bukata.

Bayanai sun nuna cewa matatar ta Dangote za ta iya tallafawa wajen kafa gidajen mai guda 26,716, da samar da ayyukan yi na kai tsaye 100,000, da kuma samar da kasuwar danyen mai ta Najeriya $21bn a duk shekara.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]