Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Yi Barazanar Fara Yajin Aiki

Kungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa ta NARD tayi barazanar tsunduma yajin aiki matuƙar gwamnatin tarayya ta gaza biya bukatun kungiyar cikin makonni biyu.

NARD ta bayar da wa’adin ne a ƙarshen taron shugabanninta na kasa ranar Asabar a Abeokuta babban birnin jihar Ogun.

Shugabannin kungiyar na kasa sun ce, gwamnatin tarayya taki yarda ta tattauna da kungiyar ko kuma ɗaukar wani kwakkwaran mataki kan kara albashin likitocin.

Har ila yau kungiyar ta zargi gwamnatin tarayya da kin biyan likitocin ariyas na shekarun 2014,2015 da kuma 2016.

Kungiyar ta kuma yi allawadai da kudirin dokar hana likitoci fita kasar waje har sai sun yi aiki a kasar nan na tsawon shekaru 5.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]