Sojoji sun kashe yan bindiga da dama a Kaduna

Jami’an tsaro sun samu gagarumar nasara a yakin da suke da yan bindiga bayan da sojojin kasa da na sama suka kashe Yan bindiga da dama a wani farmaki da suka kai a yankin Galbi dake karamar hukumar Chikun ta jihare Kaduna.

Kwamishinan tsaro na jihar Kaduna,Samuel Aruwan shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

A cewar sanarwar jami’an rundunar Operation Forest Sanity da hadin gwiwar sojojin sama sune suka kai farmaki a matartarar yan bindigar dake yankin na Galbi.

Aruwan ya bayyana cewa a yayin farmakin sai da sojojin suka tsallaka kogin Kaduna inda suka fuskanci turjiya daga yan bindigar.

Bayan dauki ba dadi ne sojoji sun samu nasarar kashe yan bindiga masu yawa tare da samun bindigogi kirar GPMG guda biyu, AK47 guda uku sai kuma baburan hawa guda bakwai.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]