Sojoji sun kashe yan bindiga da dama a Kaduna

Jami’an tsaro sun samu gagarumar nasara a yakin da suke da yan bindiga bayan da sojojin kasa da na sama suka kashe Yan bindiga da dama a wani farmaki da suka kai a yankin Galbi dake karamar hukumar Chikun ta jihare Kaduna.

Kwamishinan tsaro na jihar Kaduna,Samuel Aruwan shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

A cewar sanarwar jami’an rundunar Operation Forest Sanity da hadin gwiwar sojojin sama sune suka kai farmaki a matartarar yan bindigar dake yankin na Galbi.

Aruwan ya bayyana cewa a yayin farmakin sai da sojojin suka tsallaka kogin Kaduna inda suka fuskanci turjiya daga yan bindigar.

Bayan dauki ba dadi ne sojoji sun samu nasarar kashe yan bindiga masu yawa tare da samun bindigogi kirar GPMG guda biyu, AK47 guda uku sai kuma baburan hawa guda bakwai.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...