Amsar tambayoyinku kan nau’ukan haraji a Najeriya

  • Nabeela Mukhtar Uba
  • Broadcast Journalist

Wannan maƙala ce ta musamman bayan da muka buƙaci mabiyanmu da masu saurare su aiko da tambayoyinsu kan abin da suke son sani game da tsarin biyan haraji a Najeriya.

BBC Hausa ta duba tambayoyin naku kuma ta miƙa su ga masana da masu ruwa da tsaki a fannin na haraji.

Mene ne haraji?

Tambaya ce da muka samu daga Maruma Ibirahim da wasu da dama da ba su rubuta sunayensu ba

Dakta Shamsuddeen Muhammad, masanin tattalin arziki a Jami’ar Bayero ta Kano da ke Najeriya, ya bayyana haraji a matsayin wani kuɗi da gwamnati ta wajabta wa jama’a biya.

“Wani kuɗi ne na dolen-dole da gwamnati take ɗora wa ƴan ƙasa ko dai a kan kuɗin da suke samu a wurin sana’o’insu ko kuma a kan riba da suke samu a kasuwancinsu,” in ji shi.

Masanin ya ƙara da cewa kuɗaɗen harajin da gwamnati take karɓa suna taimaka wa gwamnatin wajen samun kuɗaɗen shiga.

Amfanin haraji

Tambaya ce da muka samu daga Mukhtar Muhammad Ngibirma da Abdulrasheed Kaku Unguwan Sarki Kaku da Nazifi Lawal Batsari da Siraja Abubakar da Ibrahim mai Indomie da Abbakar Usman

Masanin tattalin arzikin ya ce zai yi wuya a iya rarrabe amfanin haraji ga mutane da kuma gwamnati saboda “kamar gwamnatin ita ce mutane.”

Amma ya bayyana wasu kamar haka:

Samar da ayyukan more rayuwa

Bayanan hoto,
Daga cikin ayyukan da ake da kuɗaɗen haraji har da gina abubuwan more rayuwa

Masanin ya bayyana cewa ana karɓar haraji ne domin bai wa gwamnati damar gudanar da ayyukan more rayuwa ga al’ummarta kamar ruwan sha da wutar lantarki da tituna da tallafi da gwamnati ke bayarwa lokacin da aka shiga wasu matsaloli.

Rage amfani da abubuwa masu cutarwa

Baya ga samar da ayyukan ci gaba a ƙasa, masanin ya ƙara da cewa harajin yana da amfani saboda yana rage amfani da abubuwa masu cutarwa inda ya ba da misali da kamfanonin giya da taba a Najeriya, wadanda suke biyan haraji mai nauyi wanda ya kai kusan kashi 20 cikin ɗari na kayan da suke samarwa “saɓanin kashi bakwai da rabi na sauran kayan masarufi.”

Ya ce ana yin haka ne domin rage yawan shan barasa da kuma taba sigari a ƙasar, “shi haraji idan an sa wa kaya sun yi tsada sosai, lalle mutane za su rage shansu maimakon wataƙila mutum ya sha kara 10 na sigari a rana, sai ya sha kara biyu ko uku ko biyar.”

Gyara muhalli

Ana amfani da haraji wajen gyara muhalli – “duk inda masana’antu suke suna taimaka wa wajen lalacewar muhalli, ta lalata ruwan sha da iska da sauransu.

”Idan ana ɗora haraji mai nauyi kan irin waɗannan dagwalon masana’antu ke zubarwa su masana’antun suna ƙoƙarin rage abin da suke zubarwa na dagwalon wanda wannan yana taimakawa haraji ƙwarai da gaske,” in ji Dakta Shamduddeen Muhammad.

Taƙaita shigo da kaya daga ƙasashen waje

A cewar masanin, wani ƙarin amfanin harajin shi ne yana rage shigo da kaya daga ƙasashen waje domin bunƙasa kamfanonin cikin gida.

“Misali, kayan da gwamnati ba ta so a shigo da su waɗanda take ganin za a iya yinsu a cikin gida sai ta ɗora musu haraji mai yawan gaske, waɗanda idan an kawo su a cikin gida ba za su sayu ba sai dai misali sani na cikin gida,” a cewar masanin.

Gyara tattalin arziki

Ana amfani da haraji wajen cimma wannan buƙata “duk lokacin da hauhawar farashi ta yi yawa cikin ƙasa mafi yawa abin da yake faruwa kuɗi ne yake yawa a hannun jama’a sai gwamnati ta ɗora haraji a kan mutane ta rage yawan kuɗin da yake hannun mutane (ta yadda) mutane ba za su iya sayan abubuwan da suke so ba, wannan zai rage yawan buƙatar abubuwa a kasuwa.”

Ya ce a duk lokacin da aka samu buƙatar abubuwan da mutane suke so a kasuwa hakan yana sa farashi ya sauka.

A cewar masanin karɓar haraji na taimakawa wajen samar da ayyukan yi inda ya ba da misali da yadda a wani lokacin matsalar rashin aikin yi take yawa.

“A wannan lokacin abin da gwamnati take yi shi ne rage yawan haraji a kan mutane domin su samu kuɗaɗe da yawa a hannunsu da za su kashe a kasuwanni, idan sun kashe kuɗi da yawa a kasuwanni, masana’antu za su samu damar yin kayayyaki da yawa saboda akwai ciniki a kasuwa, wannan zai taimaka su ɗebi ma’aikata da yawa,” kamar yadda masanin ya shaida wa BBC.

Rage bambancin arziki tsakanin ƴan ƙasa

Ana kuma amfani da haraji wajen daidaita tsakanin ƴan ƙasa ta fuskar tattalin arziki saboda masu wadata sun fi biyan haraji mai yawa yayin da waɗanda talakawa suke biyan haraji ɗan kaɗan ko ma ba sa biya.

Ƙarin maƙaloli masu alaƙa

Masanin ya ce haraji ya rabu gida biyu – na kai tsaye da wanda ba na kai tsaye ba.

Harajin kai tsaye

Wannan haraji a Turancin Ingilishi ana kiransa Direct Tax. Wannan haraji ne da ya shafi mutum kai tsaye da zai biya daga albashinsa ko kuma idan kamfani ne zai biya daga ribarsa.

Ana kiransa haka ne saboda shi ya shafi mutum kai tsaye.

Ya ce akwai ire-iren haraji da suka faɗo a ƙarƙashin wannan nau’i na haraji kamar harajin da mutum zai biya kai tsaye daga albashinsa wato Personal Income Tax ko Pay As You Earn da kuma harajin da ake cira daga ribar kamfanoni wato Profit Tax.

A cewarsa, duk ribar da kamfani ya samu a shekara zai ware wani abu ya bai wa gwamnati wani abu cikin ribar.

Harajin da ba na kai tsaye ba

Tsarin wannan harajin shi ne mutum ba a cikin kuɗinsa zai biya ba. “Misali harajin kayayyaki da ake sana’antawa, idan mai kamfani ya biya harajin kayan da ya sana’anta zai ƙara waɗannan kuɗaɗen a kan kayan da ya sana’anta domin sayarwa,” in ji Dakta Shamsuddeen Muhammad.

Sai dai masanin ya ce a ƙarshe nauyin harajin yana ƙarewa ne a kan mai saye “wanda ya biya daban wanda kuma nauyin harajin ya faɗa a kansa daban.”

A ƙarƙashin wannan nau’i na haraji akwai wanda ake biyawa kayan masarufi wato VAT – “shi kamfanin da yake ba wa gwamnati harajin ba shi ne yake bai wa gwamnati haraji ba, kwastomomi waɗanda suke sayen kayan su ne suke biyan harajin.”

Akwai kuma harajin kuɗin fito wato Customs Duty ko Import da Export Duty- “idan mutum ya shigo da kaya na sayarwa daga ƙasar waje, zai biya musu haraji amma zai ƙara wannan haraji kan farashin kayan inda shi wanda zai kayan ya yi amfani da su shi ne wanda harajin zai ƙare a kansa,” in ji masani Dakta Shamsuddeen Muhammad.

Wannan haraji na kuɗin fito yana haura harajin VAT a Najeriya amma akwai ƙasashe na duniya musamman waɗanda suka ci gaba wanda shi harajin na VAT shi ne mafi yawan harajin da gwamnati take karɓa a kowanne lokaci.

Ya ce akwai wasu kuɗaɗen shiga da ake biya kamar tara ko kuma Levy wanda ake ɗorawa a kan amfani da kayan gwmanati kamar masu haƙar ma’adinai da ƙarafuna da gwal suna biyan kuɗin hayar ƙasa wato Royalties ko kuma Lease.

Sai kuma tara ta kotu da ake biya ko kuma idan mutum ya yi laifi a ɗora masa wata tara – “ba haraji ba ne na kai tsaye amma yana cikin kuɗaɗen shiga da gwamnati take samu,” a cewar masanin.

Harajin kayan masarufi wato VAT

Tambaya ce da muka samu daga Abbas Jobi da Abdulazeez Abubakar Baba da Nura Muhd Sani da Jamilu Bala Abdulkadir da Ibrahim mai indomie da Hussaini Mukhtar Isah Fagge da Abubakar Jidda da Farouk Ado Danmaliki da Yahaya Musa da Mustapha Magaji Muhammad

Shi wannan haraji ana biyawa kayan masarufi ne kuma kamfanonin cikin gida ne suke ɗora wannan haraji a kan kuɗin kayansu amma wannan ƙarin da suka yi na haraji ba nasu bane na gwamnati ne.

Dakta Shamsuddeen ya ce: “Idan mutane sun sayi kayan za su cire wannan kaso na haraji sai su bai wa hukumar da take karɓar haraji na gwamnatin tarayya.”

Ya ce irin wannan harajin yana daga cikin manya-manyan haraji da gwamnati take karɓa kuma ana ɗora shi a kan dukkan kayan masarufi da ake sana’antawa a cikin ƙasa ban da waɗanda gwamnati ta ga dama tace ban da su saboda wasu dalilai.

“Kamar misali mu a nan Najeriya, an ce duk abin da ya shafi kayan abinci da kayan ilimi da kayan lafiya – waɗan nan su ba za a ɗora musu harajin VAT ba amma bayan su duka sauran abubuwan da sauran ƴan ƙasa suke amfani da su har wutar lantarki duka wannan haraji na VAT yana kansu,

Yadda yake shi gwamnati tana ɗora wani kaso na kai tsaye da za ta ce komai za a sayar za a ƙara wannan kaso a kan kuɗinsa wanda shi wannan kason shi ne VAT ɗin wanda gwamnati ce za ta karɓe shi.

Misali a Najeriya yanzu, kason da ake biya na harajin VAT kashi bakwai da rabi cikin ɗari ne wanda ya ƙaru daga kashi biyar da da ake biya a wannan shekarra a watan Fabrairu aka ƙara shi daga kashi biyar cikin ɗari zuwa kashi bakwai da rasbi cikin ɗari,” in ji masanin.

Wasu labaran da za ku so ku karanta

Harajin Stamp Duty

Tambaya ce da muka samu daga Salisu Dayyabu

Masana sun ce wannan haraji na Stamp Duty ɗaya daga cikin tsofaffin harajin da ake biya a duniya kuma ya samo asali ne daga Daular Sufaniya tun ƙarni na 17 kimanin kusan shekara 400 kenan.

Hatimi ne na gwamnati da ake bugawa a kan takardu waɗanda ake amfani da su wurin wata yarjejeniya ko kuma ciniki – takardu irinsu chekin kuɗi da takardar lasisin aure ko takardar sai da filaye duka suna buƙatar gwamnati ta buga hatiminta a kai domin ya zama cewar su waɗan nan takardu sun zama masu amfani kuma ko da kotu aka je waɗan nan takardu za su iya zama shaida saboda ga hatimi na gwamnati an buga a kai.

“Duk wanda ya yi irin wannan ciniki ko kuma suka yi irin wannan yarjejeniya ko kuma suka yi irin wannan yarjejeniya har gwamnati ta buga hatimi a kai sai a biya gwamnati kuɗi na hatimin da ta buga. Amma tun wannan lokaci gwamnatoci na duniya daban-daban suna amfani da wannan tsari har muka kawo zamanin da yanzu yawanci cinikayyar ba a yin ta fuska da fuska, yawanci cinikayya ce da ake yi ta kafofin sadarwa na zamani ko ta imel ko ta sauran kafafe na sadarwa na zamani,

Sai gwamnati a baya-bayan nan ta ga cewa tun da yanzu ba a amfani da takardu na zahiri, me zai hana shi wannan Stamp Duty da ake biyawa takardu na zahiri ya koma kan har irin waɗan nan kasuwanci da ake yi ta kafafen sadarwa na zamani.

Mu a nan a Najeriya daga watan Fabrairu, gwamnati ta ƙirƙiro cewa duk musayar kuɗi da aka yi ta bankuna – wani ya tura wa wani kuɗi in dai sun kai N10,000 sai ya biya wa wannan kuɗi abin da ake cewa Stamp Duty ɗin saboda a wajen gwamnati tana ganin duk wanda ya tura kuɗi har ya kai N10,000 ko sama da haka, lalle cinikayya aka yi,” in ji masanin.

Abin da gwamnatin Najeriya take samu daga harajin VAT

Kuɗaden da gwamnati take samu daga harajin kayan masarufi suna hawa da sauka ne – ya danganta da yadda harkar tattalin arziki ta gudana a kowane wata tun da kuɗin ana karɓarsu ne wata-wata.

“A baya-baya lokacin da ake cikin wannan lalura ta Covid-19, kuɗin da ake karɓa na harajin VAT baya wuce N100bn amma a watan Agusta, kuɗaɗen da gwamnati ta karɓa ya kai sama da N150bn,

Dakta Shamsuddeen Muhammad ya ce: “Shi harajin VAT mafi yawa gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi ne suka fi morarsa, duk da cewa gwamnatin tarayya ce take karɓa amma idan an zo rabon arzikin ƙasa na wata-wata kusan kashi 86 cikin 100 na abin da aka karɓa na VAT yana tafiya ne ga gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi.

A watan Agustan da ya gabata duk da dai an karɓi kuɗi har N150bn abin da gwamnatin tarayya ta mora a ciki bai wuce N20bn, ragowar kusan N130bn an raba su ne tsakanin ƙananan hukumomi da jihohi – jihohi sun rabauta da N70bn su kuma ƙananan hukumomi suka samu abin da bai fi N60bn.”

Ina kuɗin haraji ke tafiya da yadda ake sarrafa shi?

Tambaya ce da muka samu daga Ahmed Alim da Ahmad Tukur

Akwai wani asusu da ake kira Federation Account a Turancin Ingilishi wani asusu ne da ake buɗe shi a babban bankin ƙasa wanda ake zuɓa kuɗaɗen harajin a kowane wata.

Aannan a haɗa da sauran kuɗaɗe da gwamnati take samu ta hanyar sayar da mai a tara su sai sun taru a ƙarshen wata sai a raba su tsakanin gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi, wanda kwamitin FARC da aka ɗorawa alhakin rarraba arziƙin ƙasa yake yi a kowane wata.

Game da sarrafa kuɗaɗen harajin kuma, gwamnatocin a matakan uku suna amfani da kuɗaɗen wajen biyan bashi da yi wa ƙasa hidima da samar da abubuwan more rayuwa musamman manya-manyan ayyuka irinsu tituna da sauransu.

Su wane ne suke da ikon karɓar haraji?

Masanin tattalin arzikin ya bayyana cewa akwai harajin da gwamnatin tarayya da gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi suke karɓa.

A cewarsa: “Manya-manyan haraji na ƙasa kamar wanda ake cirewa a albashi, kamar wanda ake biya na shigo da kayayyaki ko fito da su da na wanda manya-manyan kamfanoni suke biya a cikin ƙasa, waɗan nan duka gwamnatin tarayya ce take karɓarsu.”

Bayanan hoto,
Hukumar FIRS ce ke da alhakin karɓar haraji a Najeriya

Baya ga waɗannan akwai kuma wasu harajin da gwamnatin jiha da ƙananan hukumomi suke karɓa kamar harajin kasuwanni da harajin tashoshi da harajin masu sufuri da sauran abubuwa da suka danganci ƙananan haraji.

Mafi yawan ƙananan hukumomi akwai sassa da suke kula da karɓar haraji a kasuwanni ko a tashoshi ko a hannun masu sufuri sannan su ma gwamnatocin jihohi suna da ma’aikata guda da take karɓar haraji domin gudanar da ayyuka ga ƴan ƙasa.

Ita ma gwamnatin tarayya tana da babbar hukumar da take tattara mata haraji – Hukumar FIRS sai hukumar kwastam wadda take da alhakin karɓar harajin kayan fito na shige da ficen kayayyaki sannan ta miƙa su hannun hukumar karɓar haraji ta ƙasa.

Akwai kuma ƙananan ma’aikatu na gwamnati da suke karɓar haraji da tara da ake ɗorawa mutane kamar Hukumar Aika Saƙonni ta Najeriya (NIPOST) da kotuna da suke ɗora tara a kan wanda suka yi laifi da sauran hukumomi masu tsaron kan hanya.

Ita kanta kamfanin sarrafa albarkatun man fetur NNPC ita ma tana karɓar haraji na haƙar man fetur daga wajen waɗanda aka yarjewa su dinga haƙa sannan ma’aikatar kula da ma’adanai tana da alhakin karɓar kuɗin hayar ƙasa da take bai wa kamfanoni ko mutanen da suke haƙar ma’adanai a cikin ƙasa.

Duka waɗannan mafi yawa sun fi karɓar tara ko kuma kuɗin haya yayin da hukumar FIRS da ta kwastam suke karɓar haraji ka tsaye a madadin gwmanatin tarayya.” a cewar masanin.

Hanyoyin karɓar haraji

Tambaya ce da muka samu daga Idrisir abdullahi da Jabir garba kauran wali da Farouk Ado Danmaliki

A cewar masani Dakta Shamduddeen Muhammad, dangane da hanyoyin karɓar haraji, ya danganta da irin harajin inda ya ba da misali da harajin da wanda ma’aikaci yake biya daga albashinsa, idan kuma ma’aikacin gwmanati ne dama gwamnati ce ke biyan albashi kuma za ta ɗebe harajin tun daga tushe sannan ta turawa hukumar da take biyan albashi, harajin kuma sai ta turawa hukumar da take karɓar harajin.

Idan kuma kamfani ne, kowane kamfani a ƙarshen shekara zai rubuta ribar da ya samu a shekara sannan ya ware kason biyan haraji ya je ya shigar wa hukumar tattara haraji wannan kuɗi a banki, sannan ya kai shaidar cewa ga abin da ya ci riba ga kason haraji da ya biya su kuma su ba da takardar cewar ya biya haraji a wannan shekarar.

Idan ya ƙi yin hakan akwai hanyoyi da ita hukumar karɓar haraji ta ƙasa take bi don tabbatar da ta karɓi wannan haraji – tun daga amfani da jami’an tsaro har zuwa kotuna har ma a ƙarshe idan kamfani ya kasa biyan haraji a rufe kamfanin ko ma a sayar da shi kuma gwamnati ta ɗebi kuɗinta a cikin kadarorin kamfanin.

Shin gwamnati tana abin da ya dace da kuɗaɗen harajin?

Masanin tattalin arzikin ya ce ba za a ce gwamnati ba ta yin komai ba saboda “komai lalacewa a ƙalla kusan kowane wata gwmanati za ta biya ma’aikata albashi sannan abubuwan da ba a rasa ba na gudanar da gwmanati na harkokin ilimi da harkokin lafiya duka gwmanati za ta yi ko da bai kai yadda mutane suke tsammani ba.

Sai dai ya ce matsalar ita ce “ana zargin cewa idan an ware wasu kuɗaɗen domin yin wasu ayyukan a cikin ƙasa ana samun ɓatagari a cikin waɗanda suke riƙe da madafun iko ko waɗanda aka ɗorawa alhakin yin waɗannan ayyuka sai su ɗebe wani kaso na wannan kuɗaɗe da aka ware don yi wa jama’a aiki, sai su kwashe kuɗaɗen gaba ɗaya su zuba a aljihinsu ko ma a (asusunsu) kuma su ƙi yin wannan aiki ko kuma su yi shi rabi da rabi su yi shi ba yadda ya dace ba su kwashe ragowar kuɗaɗen.”

Inganta tsarin haraji da amfani da shi

A cewar Dakta Shamsuddeen Muhammad ya ce Najeriya tana ɗaya daga cikin ƙasashen da aka yi ƙiyasin cewa kuɗaɗen harajin da ‘yan ƙasa suke ƙin biya ya yi yawa saboda a shekarar 2019, shugaban hukumar karɓar haraji ya ce gwmanati tana kusan asarar naira triliyan biyar a harjin da ba a karɓa ba kuma laifin ya haɗa da mutanen da suke biyan haraji da kuma hukumomin da suke karɓar harajin.

“Su mutane dama kowa zai yi ƙoƙarin ƙin biyan haraji har sai dai idan ya ga ba yadda zai yi gwmanati ta tilasta shi, idan ya ga cewa gwmanati ba ta san da shi ba ko kuma gwmanati ba za ta san nawa ya kamata ya biya ba, wannan abu ne na rashin nuna kishin ƙasa da kuma daƙile harkar ci gaba a cikin ƙasa domin wannan haraji da mutane za su biya da shi ne gwmanati za ta yi wa mutane aiki.

Wani lokacin kuma matsalar tana faruwa ne daga hukumomin da suke karɓar harajin su ne suke haɗa baki da abokansu ko ƴan uwansu da suke da kamfanoni su nuna musu ba ma sai sun biya haraji ba su nuna musu kamar taimaka musu suke yi abin da ya kamata ka biya sai ka biya abin da bai kai rabinsa ba.

Kuma su hukumomin da suke karɓar harajin ko kuma jami’ansu sun san cewa abin da ka biya ba shi yakamata ka biya ba abin da za ka biya ya ninka haka amma sai su yi shiru saboda wata alaƙa da take tsakaninsu ko kuma saboda za ka ɗebi wani abu na wannan kaso na abin da ba ka biya ba su ma ka ba su su zuba a aljihinsu.”

Amma ya ce yadda yake ganin za a gyara lamarin shi ne kowa ya sa tsoron Allah da kishin ƙasa da son ci gaban ƙasa a zuciyarsa wanda ya ce rashin haka babbar matsala ce.

Illar rashin biyan haraji

Shiga garari

Masanin ya ce babbar illar rashin biyan haraji shi ne gwamnatin Najeriya za ta koma dogaro ne da kuɗaɗen da take samu daga sayar da mai da sauran ma’adanai – “duk sanda kuɗin man fetur ya faɗi a kasuwar duniya, ƙasar tana shiga garari tana shiga wani hali saboda mutane ba sa biyan harajin da ya kamata, kowa a ƙasar sai ya shiga wahala, tsadar rayuwa ta yi yawa, talauci ya yi yawa rashin aikin yi ya yi yawa.

Yawan ciyo bashi

Wata matsalar ta haɗa da yawan basussukan da gwamnati take ciyowa domin ta samu ta yi ayyukan da suka zama wajibi ko kuma take son yinsu.

Ya ce da gwamnati tana samun isassun kuɗaɗen harajin wataƙila da ba sai ta dangana da ciyo bashin ba.

More from this stream

Recomended