An Samu Karin Mutum 745 Da Suka Harbu Da COVID-19 a Najeriya

Hukumar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta ce adadin wadanda suka kamu da COVID-19 a kasar ya kai 18,480.

Adadin ya kai wanann matakin ne bayan da aka samu karin mutum 745 da suka kamu da cutar a jihohi 21, ciki har da Abuja babban birnin kasar.

Jihohin da aka gano sabbin wadanda suka kamu da cutar sun hada da Legas inda aka samu mutum 280, 103 a Oyo, 72 a Ebonyi, 60 a Abuja, 46 a Imo, 34 a Edo, 33 a Delta, 25 a Rivers, 23 a Kaduna, 16 a Ondo, 12 a Katsina, 10 a Kano.

Sauran jihohin sun hada da Bauchi mai mutum 8, 7 a Borno, 5 a Kwara, 4 a Gombe, 2 a Sokoto da Enugu, da kuma 1 a Osun, Nasarawa da Yobe.

Wannan dai shine adadi mafi yawa da aka samu a rana daya tun bayan da wasu jihohin kasar suka fara sassauta matakan kulle saboda dakile yaduwar cutar annobar ta COVID-19.

Sanarwar da hukumar ta fidda a shafinta na Twitter ranar Alhamis 18 ga watan Yuni ta kuma ce ya zuwa yanzu an sallami mutum 6,307 daga asibiti kana mutum 475 sun mutu.

More from this stream

Recomended