Gwamnatin jihar Neja, a ta bakin sakataren gwamnatin jihar kuma shugaban kwamitin yaki da yaduwar cutar coronavirus a jihar, Alhaji Ahmed Ibrahim Matane, ya ce zama a irin wadannan wuraren sai da hakuri, don haka jama’a su kara hakuri.
Wannan shine karo na biyu a Najeriya da aka samu aukuwar wannan lamarin bayan jihar Gombe. Masu sharhi na ganin wannan abin duba wa ne.
Masani a harkar kiwon lafiya kuma babban sakataren kungiyar bada agajin musulunci ta Nigeria, Dr. Abba Yahaya, ya ce karancin kulawa ne ke haddasa boren a irin wadannan cibiyoyin, a saboda haka akwai bukatar a kara kula da su da kyau, ko da yake ya ce yin bore ba shine mafita ba.
A halin da ake ciki dai an samu karin mutum 2 da suka kamu da cutar coronavirus a jihar Neja, yanzu mutane 5 kenan suka harbu da cutar a fadin jihar.