Coronavirus: Gwamnatin Neja ta ce a koma bakin aiki | BBC Hausa

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Latsa alamar lasifikar domin sauraron jawabin Kwamishinan yada labaran jihar Neja a tattaunawarsu da Haruna Shehu Tangaza

Gwamnatin Neja da ke tsakiyar Najeriya ta sanar da matakin sassauta umarnin hana fita da ta sanya tun bayan bullar annobar coronavirus a kasar.

Kwamishinan watsa labarai na jihar, Alhaji Sani Idris ya shaida wa BBC cewa tun da farko dai gwamnatin ta ba da umarnin hana tafiye-tafiye daga karfe takwas na safe zuwa takwas na yamma domin kare yada cutar.

A cewar kwamishinan, sauran dokokin da aka sa kamar na hana taruwa a makaranta da wuraren ibada suna nan daram.

Har yanzu dai ba a samu rahoton bullar cutar coronavirus ba a jihar duk da cewa jihar na makwabtaka da Abuja babban birnin kasar.

Ya ce gwamnati ta sha sassauta dokar hana fitar a lokuta daban-daban sakamakon bibiyar al’amuran da ke wakana a Abuja.

“Daga baya mun yi sassauci aka mayar da dokar daga karfe goma na safe zuwa takwas na dare sannan da muka ga iyakoki a bude ana shige da fice, sai muka sake mayar da dokar daga karfe goma na safe zuwa 12 na dare,”.

A cewarsa, tun daga lokacin gwamnatin jihar ta bijiro da tsare-tsare daban-daban da suka hadar da gudanar da bincike kan baki da suka shiga jihar.

“La’akari da yadda al’umma suka ba da goyon baya muka ga ya kamata a kara sassauta dokar,”. Kwamishinan ya ce matakin zai bai wa gwamnati damar fito da tsare-tsare masu muhimmanci.

“Akwai umarni da aka ba shugabannin ma’aikatun da za a bude, kowace ma’aikata za a tanadi abubuwa da ma’ikatan lafiya suka ba da shawara yadda za a wanke hannu da kiyaye cunkoso.”

“Matakin dakatar da tafiye-tafiye tsakanin makwabtan jihohi zuwa Neja har yanzu yana nan.”

More from this stream

Recomended