
Hakkin mallakar hoto
Reuters
—BBC Hausa
Kungiyar Tarayyar Turai ta nuna bacin rai kan yadda masu zanga-zangar kin jinin gwamnati ke tayar da hankali
Kan shugabannin kasar Albaniya ya rabu a kan zaben kananan hukumomi da za a yi a karshen makon nan, lamarin da ya kara rura wutar dambarwar siyasar kasar.
Yayin da Shugaban kasar Ilir Meta ya bayar da umarnin a dage zaben har zuwa watan Oktoba, shi kuwa Firaminista Edi Rama kekasa kasa ya yi ya ki amincewa da dagawar, ya ce lalle sai ya gudanar da zaben kamar yadda aka tsara tun farko.
Daman tuni ‘yan jam’iyyun hamayya sun kaurace wa zaman majalisa, inda suka shafe watanni suna zanga-zangar kin jinin gwamnati.
Kauracewar da suka yi wa zaben kananan hukumomin ta tilasta matsar da zaben shugaban kasar, kamar yadda Mista Meta ya ce zanga-zangar ta hamayya da gwamnati da kauracewar ‘yan hamayya, ba za su sa a samu zaben ya kasance cikin gaskiya da adalci ba.
Sai dai Firaministan ya dage, inda ya tsaya kai da fata kan matsayarsa, ya ki amincewa da dagewar, dadin dadawa ma har ya dauki matakin fara shirin tsige Mista Meta.
Shi kuwa Shugaban ko gezau, sai ma ya sanya lokacin zaben zuwa ranar 13 ga watan Oktoba a yanzu, duk da cewa gwamnati da hukumar zabe sun kafe cewa ranar Lahadin nan za a fara zaben.
Hakkin mallakar hoto
Reuters
A baya Albania ta nuna bukatarta ta shiga kungiyar Tarayyar Turai
Wannan kuma ya sa jagororin ‘yan hamayya suka lashi takobin daukar matakin hana yin zaben.
‘Yan hamayyar sun zargi Firaminista da shirin yin magudi da kuma almundahana, wanda a kan haka tun da farko suka bukaci a yi zabe na wuri.
Haka kuma suna son ganin an kafa gwamnatin rikon-kwarya, inda suka ki zaman tattaunawa domin samun daidaito da Firamoinistan.
Shugaban jam’iyyar hamayya ta Democratic Party Lulzim Basha, ya bukaci masu zanga-zanga da su ci gaba har sai Mista Rema ya sauka daga mukaminsa.