2023:Ahmad Lawan ya roƙi ƴan Najeriya su sake bawa jam’iyar APC dama

Shugaban majalisar dattawa sanata, Ahmad Lawan ya roki yan Najeriya da su sake bawa jam’iyar APC dama a zabe mai zuwa.

Ya fadi haka ne a wurin taron jin ra’ayin jama’a da sanata mai wakiltar mazabar Kwara ta tsakiya, Dr Ibrahim Yahaya Oloriegbe ya shirya a ranar Asabar.

A wurin taron da ya gudana a birnin Ilorin Oloriegbe ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara.

Tun da farko sai da shugaban majalisar dattawan ya kaddamar da wasu ayyukan raya kasa da sanatan ya samar a mazabarsa.

Amma kuma Lawan ya gargadi mutanen jihar da su kaucewa dawo shugabannin da suka mulki jihar a baya.

“Ina son na yi kira ga dukkanin yan Najeriya da su sake bawa jam’iyar APC dama a dukkanin mataki har bayan 2023. Munyiwa yan Najeriya alkawarin cigaba da yin bakin ƙoƙarin mu. Kuma baza mu saɓa ba.”

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...