Ƴan majalisar dokokin jihar Zamfara 7 sun dakatar da abokan aikinsu 16

Bakwai daga cikin yan majalisar dokokin jihar Zamfara 24 sun dakatar da yan majalisar jihar su 16 da ake zargin sun yi yunkurin tsige kakakin majalisar dokokin jihar,Bilyaminu  Moriki.

A ranar Juma’a ne mambobin majalisar su 16 suka sanar da matsayar da suka dauka ta dakatar da Moriki saboda tsawon lokacin da ya É—auka baya jihar duk da cewa jihar na fama da hare-haren Æ´an fashin daji.

Dakatarwar ta biyo bayan kuɗirin da Nasiru Abdullahi mamba mai wakiltar mazaɓar Maru ya gabatar.

Mambobin sun kuma naɗa Bashar Gummi a matsayin kakakin majalisar na riƙo.

A yayin zaman majalisar na ranar Litinin majalisar ƙarƙashin jagoranci  Moriki ta ayyana zaman da waɗancan ƴan majalisar dokokin suka yi a matsayin haramtacce.

Sun yi kira ga mutanen jihar da su yi watsi da labaran da ake yaÉ—awa na dakatar da shugaban majalisar.

Ƴan majalisar sun yi zargin cewa wasu manyan ƴan siyasa dake zaune a wajen jihar su ne ke ɗaukar nauyin abokan aikinsu domin su kawo tangarɗa ga gwamnatin,Dauda Lawal Dare.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...