Ƴan majalisar Bauchi na farautar wanda ake zargi ya yi wa ƴar shekara 7 fyaɗe

rape victim

Majalisar Bauchi ta shiga farautar wani da ake zargi ya yi wa wata yarinya yar shekara bakwai fyaɗe.

Wasu ƴan majalisar sun yi zargin cewa an bayar da mutumin mai shekara 45 beli bayan kama shi.

Lamarin ya faru ne a Faggo da ke ƙaramar hukumar Shira a jihar ta Bauchi.

Ɗan majalisar da ke wakiltar yankin Honarabul Bello Muazu Shira, wanda ya gabatar da kudirin gaban majalisa ya yi kiran a gaggauta kama mutumin kan zargin yi wa ƴar shekara bakwai fyaɗe.

“Ya yi wa yarinyar barazana da makami ya yi mata fyaɗe,” in ji shi

Ɗan majalisar ya shaida wa BBC cewa majalisa ta kafa kwamiti domin tabbatar da an kama mutumin.

Ya ce sun kama hanya zuwa Shira kuma a cewarsa “zamu ta fi har garin Faggo inda yarinyar take.”

Ya kuma ce za su tattauna da shugaban ƙaramar hukumar Shira da jami’an ƴan sanda domin tabbatar da an kama mutumin.

Sai dai ɗan majalisar ya ce ba su san inda mutumin da ake zargi yake ba a yanzu. Amma ya jaddada cewa majalisa za ta tabbatar da an gurfanar da shi a gaban shari’a domin zama darasi ga masu aikata fyaɗe.

Matsalar fyaɗe dai musamman ga yara ƙanana ta zama ruwan dare a Najeriya. Kuma an sha bayar da rahoton fyaɗe a jihar Bauchi

Wannan ne ya sa gwamnatin jihar Bauchi ta kafa wata doka da ta kira VAPP wadda a turance ake kira Violence Against Persons Prohibition, ta kuma tanadi hukuncin kisa ta hanyar rataya ga duk wanda aka samu da laifin yi wa yara kanana Fyaɗe.

Haka ma dokar ta tanadi ɗaurin rai da rai ga wanda ya yi wa babbar mace fyaɗe, da kuma ɗaurin shekaru 20 ga waɗanda suka yi wa mace daya taron dangi.

Hukumomin ƴan sanda a jihar sun ce sun sha samun rahotannin aikata fyaɗe a jihar.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...