Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin da daddare a ƙofar gidansa dake Ilukpa, Iyara inda ƴan bindigar suka riƙa harbi sai kace sojoji a filin daga kafin su yi awon gaba da shi.

Mr E.K Adebayo jami’in hulda da jama’a na Kungiyar Cigaban Iyara ya bayyana rashin dacewar yin garkuwa da limamin musamman a wannan lokacin na watan Azumin Ramadan.

Ya yi kira ga hukumomin da suka da ce da su  tabbatar an sako malamin addinin.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Kogi, William Aya ya tabbatar da faruwar lamarin.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...