Ƴan sanda sun kama wasu sojan gona biyu

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta ce ta kama ta ce ta kama wasu sojan gona guda biyu Jonathan Yahaya da Muhammad Umar.

Benjamin Hundeyin mai magana da yawun rundunar shi ne ya bayyana haka a ranar Laraba.

Hundeyin ya ce wani soja mai muƙamin manjo ne dake barikin soja ta shiya ta 81 da ake kira Nigerian Army Provost, Bonny Camp, Victoria Island, Lagos shi ne ya kai mutanen biyu ofishin ƴan sanda na Onikan bayan da aka kama su.

Mai magana da yawun rundunar ya ce  sojoji sun kama ɗaya daga cikin mutanen ne sanye da wandon kakin soja da kuma takalmi a yayin da ɗayan kuma aka kama shi sanye da kakin soja.

“Biyo bayan tambayoyi an gano cewa dukkanin mutanen biyu sojan gona ne. Sun gaza faɗar yadda suka mallaki kakin soja  shine dalilin kama su.” a cewar Hundeyin.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...