Ƴan Boko Haram sun kashe manoma a Borno

Mayakan Boko Haram sun kashe manoma 10 tare da yin garkuwa da wasu da dama a karamar hukumar Mafa da ke jihar Borno.

Baya ga wannan harin da aka kai da yammacin ranar Asabar a filayen dake tsakanin kauyukan Bulakunkumma da Maiwa na gundumar Baram Karowa ta karamar hukumar, ‘yan ta’addan sun kuma samu N4m daga hannun wani dan kasuwa a unguwar Zannari a matsayin kudin fansa.

Wata majiya mai tushe, Ya Kalu Bukar, wacce ta tabbatar da harin, ta bayyana adadin wadanda aka sacen a matsayin hudu, amma wata majiya mai suna Goni Mohammed ta ce an sace mutane har tara.

“Sun zo zagayawa cikin gonaki don neman abinci da tsabar kudi,” a cewar Bukar.

“Lokacin da manoman suka ce ba za su iya biyan kudaden da suka nema ba, sun kashe 10 daga cikinsu, dukkansu maza, suka tafi da hudu.”

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...