Ƴan bindiga sun yi awon-gaba da sama da mutum 150 da shanu 1,000 a Gobir kwanaki kaɗan bayan kashe sarkinsu

Rahotanni daga Arewa maso Yammacin Najeriya na nuna cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 150 tare da sace shanu sama da 1,000 a kauyukan da ke masarautar Gobir ta jihar Sokoto.

Idan ba a manta ba, an yi garkuwa da Sarkin na Gobir, Alhaji Isa Muhammad Bawa, kuma Hakimin Gatawa a ranar 29 ga watan Yuli tare da dansa da wasu mutane shida a hanyar Sokoto zuwa Sabon Birni.

Wani faifan bidiyo mai daure kai ya nuna Sarkin yana rokon a biya masa kudin fansa kafin rasuwarsa, lamarin da ya kai ga zanga-zanga a yankin da kuma dokar hana fita a Sabon Birni.

Masu aiko da rahotanni sun tattaro cewa ayyukan ‘yan fashin na baya-bayan nan ya sake sanya damuwa kan ayyukan da suke yi a yankin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, SP Ahmad Rufa’i, ya bayyana cewa ba a samu wani rahoto a hukumance ba amma za su ci gaba da bincike kan lamarin.

More from this stream

Recomended