Zulum Ya Gargadi Jama’a Kan Sauran Yan ta’adda A Maiduguri

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya bayyana cewa sun samu sahihan bayanan sirri da ke nuna cewa akwai sauran mahara biyu a cikin birnin Maiduguri da ke shirin kai harin ƙunar baƙin wake kan jama’a.

Gwamnan ya ce, bisa bayanan da hukumomi ke da su, mahara biyar ne suka shiga Maiduguri domin kai hari. Ya ce uku daga cikinsu sun mutu a harin da aka kai ranar Litinin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 20, yayin da ake ci gaba da neman sauran biyun.

Rahotanni sun ce maharan sun tayar da bama-bamai a kusa da asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri, da babbar kasuwar ‘Monday Market’, da kuma ofishin gidan waya a cikin birnin.

Hare-haren sun faru ne jim kaɗan bayan wasu mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare kan sansanonin sojin Najeriya a Ajari da Baga da kuma Damboa, duk a jihar Borno.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]