Za a Koma Yin Shari’ar Ta’addanci A Asirce – Babbar Kotun Najeriya

Alkalin babbar kotun tarayya a Najeriya, John Tsoho ya fitar da wata sanarwa mai taken “sabbin shawarwarin aiki kan sauraron kararrakin ta’addanci” da ke bayyana yadda kotun za ta rika gudanar da shari’un da suka shafi ta’addanci a gaban kotun.

Ya ce an tsara sabon hukuncin ne domin tabbatar da tsaron dukkan bangarori, daga masu laifin da ma jama’a da kuma tabbatar da adalci.

A gefe guda kuma, jagoran haramtacciyar kungiyar ‘yan awaren da ake zargi da laifukan ta’addanci ya shigar da kara yana zargin cewa ba za a iya yi masa shari’a ba saboda an tasa keyar sa daga Kenya ba bisa ka’ida ba, kamar yadda takardun kotu suka nuna.

Nnamdi Kanu shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) ya bace ne daga Najeriya bayan ya tsallake beli a shekarar 2017.

An kama shi bayan shekaru da dama yana gudu. Lauyansa ya ce a shekarar da ta gabata an zalunce shi a tsare a Kenya kafin a mayar da shi Najeriya, lamarin da Babban kwamishinan na Kenya ya musanta.

Lauyan Kanu, Mike Ozekhome, a ranar Alhamis, ya ce ba za a iya yi masa shari’a kan zargin ta’addanci da yada labaran karya da sane ba saboda ba a mika shi ga Najeriya ba bisa wadannan tuhume-tuhumen.

Ozekhome yana rokon kotu da ta bayyana tsare shi a matsayin haramtacciyar doka. Har ila yau karar na neman diyyar naira biliyan 50 (dala miliyan 120) da kuma naira miliyan 100 na kudaden shari’a.

A ranar Juma’a ne ake sa ran wata kotu na daban za ta yanke hukunci kan tuhume-tuhume 15 da ake tuhumar Kanu, wadanda za su iya kawo karshen shari’arsa idan har alkali ya amince da bayannan na lauyansa.

Kanu bai yarda da duk wasu tuhume-tuhumen da ake masa ba.

Kungiyar IPOB, wacce Kanu ya kafa a shekarar 2014, na neman ballewar yankin kabilar Igbo, wadda ta mamaye yankin kudu maso gabashin Najeriya. Hukumomi suna kallon IPOB a matsayin kungiyar ta’addanci. IPOB ta ce tana son samun ‘yancin kai ne ta hanyoyin da ba na tashin hankali ba.

More News

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...