‘Yan sanda sun kashe wasu matasa biyu a Kano – AREWA News

An zargi jami’an yan sanda da kashe wasu matasa biyu, Ibrahim Isa wanda aka fi sani da Banufe da kuma Ibrahim Sulaiman wanda ake kira da Mainasara a unguwar Sharada dake Kano.

Lamarin ya faru ne ranar Asabar da karfe 11 na dare a rumfar wani mai sayar da Indomie dake kusa da babban masallacin Juma’a na Sharada.

Rahotanni sun bayyana cewa hatsaniya ta barke a wurin da bayan da Mainasara ya bukaci dalilin da yasa jami’an tsaron suka zo kama kaninsa mai suna Gaddafi

Daya daga cikin yan sandan mai suna Ado shi ne yayi kokarin jawo Mainasara daga cikin shagon har ta kai ga ya caka masa wuka har sau biyu inda ya fara zubar da jini nan take.

Kokarin da mutane su kai na kawo masa dauki ya sa jami’an yan sanda harbi inda aka samu Banufe kuma ya mutu nan take.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...