‘Yan Boko Haram Sun Kai Hari Banki Dake Jihar Borno – AREWA News

An fafata a tsakanin mayakan kungiyar Boko Haram da dakarun soji a Banki, wani gari dake kan iayakar kasar Kamaru da Nijeriya.

Jaridar HumAngle ta rawaito cewa dakarun rundunar soji sun samu nasarar dakile harin da aka kai garin Banki da ke karkashin karamar hukumar Bama a jihar Borno.

Garin Banki, mai nisan kilomita uku kacal daga iyakar Najeriya da kasar Kamaru, ya kasance cibiyar ayyukan kungiyoyin jin kai.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]