Yan bindiga sun kashe wani mutum tare da sace dabbobi a Katsina

Yan bindiga sun kashe wani mutum mai suna, Rabilu Tukur dake kauyen Dan Ali karamar hukumar Danmusa ta jihar Katsina a ranar Lahadi.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa an kashe marigayin ne da misalin karfe 1 na rana.

Wani mazaunin Dan Ali da ya nemi a boye sunansa ya fadawa wakilin jaridar Daily Trust cewa marigayin wanda ma’aikacin karamar hukumar Danmusa ne na dawowa ne bayan ya sauke wani mutum a kauyen Tashar Biri.

“Yana amfani da babur dinsa wajen yin acaba inda ya kai fasinja kauyen Tashar Biri yana kan hanyarsa ta dawowa ne lokacin da maharan suka biyo shi suka farmasa da adda a kusa da kauyen Dan Ali da tsakar rana,” ya ce.

Ya kara da cewa yan bindigar sun bi sahun wasu da suka yi kaura ya zuwa kauyen na Dan Ali inda suka kwace musu dabbobi da dama.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...