Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya fitar da sanarwa bayan ganawarsa da babban hafsan sojin Pakistan, Janar Asim Munir, inda suka tattauna muhimman batutuwa kan tsagaita wuta.
Sanarwar ta bayyana cewa ganawar ta mayar da hankali ne kan “batutuwa masu muhimmanci dangane da yarjejeniyar tsagaita wutar” tsakanin Iran da Amurka.
Haka kuma, Araghchi ya yi wa Pakistan bayani kan matsayar Iran da kuma shawarwarinta dangane da hanyoyin kawo ƙarshen rikicin.
A nasa ɓangaren, Janar Asim Munir ya jaddada cewa Pakistan a shirye take ta ci gaba da rawar da take takawa wajen shiga tsakani domin samar da zaman lafiya.
Iran Da Pakistan Sun Tattauna Kan Tsagaita Wuta Da Kuma Shiga Tsakani

