Barayi yan bindiga dake kan babura sun farma kauyen Abaya dake kan hanyar Wurma a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa.
Barayin da suka farma kauyen ranar Laraba da daddare ana zargin sun harbe kusan mutane sama da 30.
Har ya zuwa lokacin da jaridar Daily Trust ta wallafa labarin babu cikakken bayanai kan adadin mutanen da abin ya rutsa da su.
Amma wasu majiyoyi sun bayyana cewa an kashe wasu mazauna kauyen yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon raunin harbin bindiga.