Yadda bindigar shaida ta harbe lauya a kotu | BBC Hausa

Bindigar da aka kai kotu shaida
Image caption

An kai bindigar otu makare da harsashi a ciki

‘Yan sanda a Afirka ta Kudu sun ce wata lauya ta gamu da ajalinta, a lokacin da harsashi ya kufce bisa kuskure daga bindigar da aka kawo kotu dan kafa shaida da ita a yankin KwaZulu Natal.

Lauyar mai suna Adelaide Ferreira-Watt ta gamu da ajalinta jim kadan bayan harbin da bindigar ta yi ma ta a kwankwasonta.

Kunamar bindigar ta dana kanta a dai-dai lokacin da aka gabatar da ita a matsayin shaida gaban alkali kan fashi da makami da aka yi a wani gida,

‘Yan sanda sun ce su na gudanar da bincike kan mutuwar Miss Ferreira-Watt a matsayin kisa ba da gangan ba.

Za kuma su yi bincike kan dalilin da ya sa aka kawo bindigar kotu alhalin akwai harsashi a cikinta, dan hakan ya sabawa ka’ida.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...