Ya kamata Buhari ya tsige shugaba Kwastam, Hameed Ali – ‘yan kasuwar Kano

Wasu ‘yan kasuwar Singer da ke birnin Kanon Dabo, sun mika koko bara na neman shugaban kasa Muhammadu Buhari, da ya tsige shugaban hukumar hana fasa kwauri ta Najeriya, Kanal Hameed Ali mai ritaya.

Shugaban kungiyar matasan ‘yan kasuwa ta Northern Young Marketers, Muhammad Bala Hotoro, shi ne ya yi wannan kira yayin hirarsa da manema labarai na jaridar Kano Today a ranar Alhamis ta makon da ya gabata.

Alhaji Hotoro wanda ya yi ikirarin cewa, wa’adin Kanal Ali a bisa kujerar jagorancin hukumar hana fasa kwauri ta kasar ya zo karshe tun a ranar 27 ga watan Agusta, bai yi wa ‘yan kasuwar Arewa da kuma kasuwancin su adalci ba.

“Muna rokon shugaba Buhari ya nada matashi kuma wanda ya cancanta daga hukumar cikin jami’an hukumar kwastam, wanda ke da kyakkyawar masaniya ta al’amurran hukumar domin ci yar da kasar nan gaba da kuma bunkasar tattalin arziki.” inji Alhaji Hotoro.

Alhaji Bala ya bayyana takaici gami da damuwa dangane da yadda da yawa daga cikin ‘yan kasuwar Arewa suka fada kwatami da kuma samun karayar arziki a sanadiyar muzgunawa ta shugaban hukumar kwastam.

Ya yi babatun cewa, Kanal Ali na neman janyo durkushewar tattalin arzikin kasar nan a sanadiyar rashin yin gwanjon kayayyaki na fasakauri da hukumar kwastam ta cafke a tashohinta, lamarin da ya ce gwamnati za ta yi asarar miliyoyin dukiya mai tarin yawa.

Haka zalika Mr Hotoro ya zargi Hameed Ali da rashin bayyana kadarori da dukiyar da ya mallaka a gaban kotun tabbatar da da’ar ma’aikata.

A sanadiyar hakan ne ya ke kira ga dukkanin masu yi wa Najeriya kyakkyawan fata, da su hada hannu-da-hannu wajen rokon shugaba Buhari a kan kada ya tsawaita wa’adin shugaban na hukumar Kwastam a bisa kujerar jagoranci.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...