Wani likitan bogi ya shiga hannun ‘yan sanda

Rafiu Ibrahim likitan bogi dake gudanar da wani haramtaccen asibiti ya fada hannun jami’an yan sanda dake aiki a sashen binciken manyan laifuka na rundunar yansanda shiya ta 11 dake Osogbo.

Mutumin da ake zargi wanda ke da shedar takardar kammala sakandare ya shafe lokacin mai tsawo yana gudanar da asibitin a wani gidan kasa mai daki daya inda yake duba marasa lafiya dake da cutuka daban-daban.

Bayanan sirri sun nuna cewa likitan bogin ya dade yana kwantar da marasa lafiya tare da zubar da ciki da kuma maganin cututtuka da suke da wuyar sha’ani inda yin hakan ke jefa rayuwar mutane cikin hatsari.

Mutumin da ake zargin ya amince da aikata laifin amma ya dora alhakin haka kan rashin aikin yi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]