Tsawa ta kashe yara 10 da ke wasan ƙwallo a Uganda

Stock image of lightning

Tsawa ta kashe yara 10 a garin Arua da ke arewa maso yammacin Uganda. An kwana biyu ana zabga ruwan sama a yankin tare da walƙiya da tsawa.

Ruwan da aka yi mai ƙarfi a ranar Alhamis ya ja yaran suka bar ƙwallon ƙafar da suke bugawa domin rakuɓewa ƙarƙashin wata bukka.

Ana cikin ruwan ne sai tsawa ta faɗa kan bukkar. Yara tara da ke tsakanin shekara 13 zuwa 15 suka mutu nan take, sai kuma ɗayan yaron ya mutu a hanyar kai shi asibiti.

Yara uku da suka tsira na jinya a wani asibiti da ke yankin.

Yankin arewacin Uganda na fama da ruwan sama kamar da bakin-ƙwarya da ke tafe da tsawa da walƙiya.

Makamancin wannan lamarin shi ne ma fi muni da ya faru a Uganda tun bayan makamancin hakan da ya faru a 2011, lokacin da yara 18 suka mutu a lokacin daukan darrusa a makaranta.

A wannan shekarar, mutum 28 sun sake mutuwa bayan sake wata tsawar duk a cikin mako guda.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...