Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai yi wa yan Najeriya jawabi kan domin bikin ranar yancin kan Najeriya.
A wata sanarwa ranar Asabar, mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya ce Tinubu zai yi wa yan Najeriya jawabi ranar Asabar.
Sanarwar ta shawarci gidajen rediyo da Talabijin da su jona kai tsaye da tashar talabijin ta NTA da gidan Rediyon Najeriya.
A ranar Lahadi ne Najeriya ke cika shekaru 63 da samun mulkin kai daga Turawan mulkin mallaka na Birtaniya.