
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na nemo hanyoyin da za su kawo ƙarshen ta’addanci da ayyukan ’yan bindiga a ƙasar nan.
Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin jawabin buɗe taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) kan bunƙasa tattalin arziƙi mai haɗa kai da ci gaban ƙasa mai ɗorewa, wanda ke gudana a Abuja.
Shugaban ya kuma yaba wa wasu gwamnonin jihohi, musamman na Borno, Katsina da Kaduna, bisa rawar da suke takawa wajen kare ’yanci da tsaron ƙasa.