Siyasa da addini ne ‘suka hana shawo kan rikici a Kudancin Kaduna’ | BBC Hausa

El Rufai

A jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya masu ruwa da tsaki na ci gaba da nuna damuwa kan rikice-rikice masu nasaba da kabilanci da addini da suka addabi yankin kudancin jihar.

Tsohon mataimakin gwamnan jahar Barnabas Bala Bantex ya shaida wa BBC cewa ana amfani da siyasa wurin raba kan al’umma, wanda ke ci gaba da rura wutar rikicin addini da na Æ™abilanci.

Ya ce ba shakka akwai mutanen da ke amfani da rikicin don samun riba a siyasar su.

Tsohon mataimakin gwamnan ya ce yana takaicin baza sojoji a kudancin jahar, wanda a cewar sa hakan zai hana ‘yan kasuwa shigowa jahar don zuba jari.

A kan haka yake ganin dole ne masu ruwa da tsaki a cikin al’umma su hadu wuri É—aya don samar da mafita.

Kaduna na É—aya daga cikin jihohin Najeriya mafi fama da matsalolin tsaro kama daga hare-haren ‘yan fashin daji a yankin Birnin Gwari da kuma rikicin Æ™abilanci musamman a yankin Kudanci.

Kimanin shekara 40 ke nan ake ta fama da wannan rikici na Kudancin Kaduna, kuma lamarin na so ya gagara.

Ko a baya-bayan nan, rahotanni sun ce an kashe gomman mutane a rikicin ta hanyar kai hare-hare masu kama da na sari-ka-noƙe a yankin.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...