Nuhu Ribadu Ya Raka ‘Yarsa Fatima Gidan Mijinta

VOA Hausa

A karshen makon nan aka daura auren Fatima da Aliyu Atiku, da ga tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar.

“Yanzu na sauke ‘yata Fatima a sabon gidanta. Abu ne mai matukar sosa rai ga mahaifi idan ya zo sauke wannan nauyi.” Ribadu ya ce a shafinsa na Twitter.

A sakon nasa Ribadu, wanda ya taba tsayawa takarar shugaban kasa, ya kuma mika godiyarsa ga daukacin wadanda suka yi tururuwar zuwa bikin auren.

“Ina mai matukar nuna godiya ga wadanda suka halarci bikin da irin karamci da aka nunawa iyalina da wadanda suka aika sakon fatan alheri da addu’o’i.” Ribadu ya kara da cewa.

Auren, wanda aka daura a Abuja babban birnin Najeriya, ya samu halartar manyan shugabannin kasar, irinsu tsohon gwamnan jihar Legas Bola Ahmed Tinubu, tsohon gwamnan Kano Dr. Rabiu Musa Kwankwaso da gwamna mai ci a jihar Yobe Mai Mala Buni da dai sauransu.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]