Muhammad Jamal wanda aka fi sani da “White Nigerian” ya yi karin bayani a kan wannan inkiyar.
Ya bayyana cewa duk da launin fatarsa shi dan asalin garin Jos ne da ke tsakiyar Najeriya, amma kakansa na wajen mahaifiyarsa dan asalin kasar Lebanon ne kuma matarsa ‘yar Columbia ce.
Muhammad ya ce saboda hada dangi da mutane daban-daban za a iya kiran gidansu “Majalisar Dinkin Duniya. “