Ministoci:Buhari ya tura sunayen mutane 7 ga Majalisar Dattawa

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya tura saunayen mutum bakwai zuwa Majalisar Dattawa a matsayin wanda za a nada sabbin ministoci.

Sunayen mutanen na ƙunshe ne cikin wata wasika da fadar shugaban kasar ta tura ga majalisar dauke da sunayen mutanen wadanda za a tantance su kafin tabbatar musu da mukaman.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023 wa’adin mulkin Buhari zai kare.

Sunayen mutanen da Buhari ya tura majalisar sun hada da Henry Ikechukwu Iko (Abia) Umar Ibrahim El-Yakub (Kano) da kuma Joseph Ukama (Ebonyi.)

Sauran sun hada da Umana Okon Umana (Akwa Ibom) Adewole Adegoroye (Ondo) Odum Udi (Rivers) da Goodluck Nnana Opia (Imo.)



Anan gaba kadan ne majalisar za ta saka rana domin tantance mutanen.

More News

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...

Mayaƙan ISWAP 73 sun miƙa wuya ga sojoji a jihar Borno

Mayakan kungiyar ISWAP su 73 tare da iyalinsu ne suka mika kansu ga sojojin shiya ta ɗaya na rundunar Operation Haɗin Kai dake Borno. A...

Gwamnonin APC sun ziyarci Tinubu

A ranar Juma’a ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya yi wata ganawar sirri da gwamnonin jam’iyyar All Progressives Congress, APC. Shugaba Tinubu a wani...

Tinubu ya naɗa shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa da sakataren gwamnatin tarayya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya naɗa kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa. Tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa, Ibrahim...