Majalisar dokokin Najeriya ta gabatar da kuduri kan jakuna

Jaki

‘Yan majalisar dokoki a Najeriya sun gabatar da wani sabon kudurin doka da nufin bai wa Jakuna kariya daga safarar su da ake yi zuwa kasashen ketare.

A jiya majalisar wakilan kasar ta amince da kudurin dokar haramta safarar jakunan karon na biyu inda kuma take shirin gudanar da zaman jin ra’ayoyin jama’a kan batun.

Abdullahi Balarabe Salame, dan majalisa mai wakiltar mazabar Gwadabawa da Illela na jihar Sokoto, ya shaidawa BBC cewa daman wannan lamari daman ya dade ya na ciwa al’umar kasar tuwo a kwarya musamman a yankuna karkara da suka fi amfani da jakunan a matsayin abin sufuri.

Ana amfani da jakuna dan aikin gona, ko dora masa kaya zuwa kasuwa da debo ruwa a rafi, a wasu lokutan akan yi amfani da shi dan daukar marasa lafiya kamar mata masu juna biyu da kauyuka zuwa bakin hanya dan kai su asibiti.

Sai dai a yanzu jakunan na fuskantar barazanar safarar su zuwa kasashen waje, musamman kasar China da suke amfani da fatar sa dan yin wasu magungunan gargajiya.

Haka kuma ana amfani da kitsen sa wajen hada mayukan shafawa da mata ke amfani da su da akai amanna da cewa su na boye stufa wato maida tsohuwa yarinya.

‘Yan majalisar na fatan da zarar an amince da dokar an kuma fara aiki da ita, za a fitar da jadawalin yadda za ta kasance da hukuncin da aka tanadar ga wanda duk ya take ta.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...