Majalisar dattawa ta dage zamanta na yau

Majalisar dattawa ta dage zamanta na ranar Talata saboda karancin halartar yan majalisar.

Philip Tanimu Aduda,sanata mai wakiltar birnin tarayya Abuja shine ya gabatar da kudurin dage zaman majalisar bisa dogaro da sashi na 10(3) da ya ce yan majalisar baza su zauna ba matsawar suka gaza kaiwa mafi ƙarancin wakilan da doka ta tanada.

Sanatoci 38 ake bukata kafin majalisar ta zauna ta tattauna kan wani batu.

Aduda ya bayyana cewa majalisar ta kasance babu sanatoci saboda yawancin su suna sassa daban daban na kasar na suna duba ayyuka.

Sanatoci kasa da 20 ne dai suka halarci zaman na yau.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]