La Liga: Varane ya ceci Real Madrid a hannun Huesca

Raphael Varane

Raphael Varane ya ci wa Real Madrid ƙwallo biyu, inda ta doke Huesca da ke ƙasan teburin La Liga a wasan mako na 22.

Nasarar ta taimaka wurin sauƙaƙa matsin lambar da ke kan mai horarwa Zinedine Zidane bayan Levente ta casa tawagar tasa har gida a makon da ya gabata.

Zidane ya buÆ™aci ‘yan jarida da su “tsahirta masa” kafin wasan na yammacin Asabar, yana mai cewa Æ™ungiyarsa na kan hanyar lashe La Liga.

Javi Galan ne ya fara zira ƙwallo a ragar Madrid minti takwas da dawowa daga hutun rabin lokaci, kafin ɗan bayan Faransa Varane ya farke a minti na 55.

Ɗan wasan mai shekara 27 ya ƙara ta biyun ne bayan an bugo bugun tazara, inda ya buga ta zaren da yake kusa da shi.

Real, wadda ke matsayi na biyu a teburi, tana bin bayan Atletico Madrid ne da tazarar maki bakwai, sai dai Atletico na da kwantan wasa biyu.

Wasa É—aya kacal Real ta ci daga cikin biyar na baya-bayan nan da ta buga, abin da ya sa ‘yan jarida suka yi wa É—an Æ™asar Faransan ca.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...