Kotun daukaka kara ta tabbatar da takarar Uba Sani

Kotun daukaka kara dake Abuja ta tabbatar da Sanata Uba Sani a matsayin dantakarar gwamnan jihar Kaduna karkashin jam’iyar APC a zaben 2023.

Sani wanda a yanzu shi ne sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya samu tikitin takara ta hanyar sulhu.

Rashin gamsuwa da yadda aka fitar da dantakarar ne ya sa, Sani Sha’aban daya daga cikin masu takara ya garzaya kotu inda yake kalubalantar nasarar da Uba Sani ya samu.

A cewar sa an gudanar da zaben ne ba tare da wakilai masu kada kuri’a ba.

Amma kuma kotun tarayya dake Kaduna tayi watsi da karar inda ta ce bata da hurumin sauraron shari’ar.

Hakan ya sa ya daukaka kara ya zuwa kotun daukaka kara dake Abuja inda ita ma tayi da karar.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...