Kasuwar musayar ‘yan kwallo: Lokaci na kurewa Man Utd da Arsenal | BBC news

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Paris St-Germain ta shiga gaban Juventus a yunkurin sayen dan kwallon Tottenham Danny Rose kuma suna fatan kammala cinikin kan fan miliyan 20, in ji jaridar (Sun).

ShugabanTottenham Daniel Levy na son daga farashin dan wasan baya Toby Alderweireld zuwa fam miliyan 40 idan har babu wanda ya sayi dan wasan a kan fam miliyan 25 nan da ranar Juma’a kamar yadda kwantiraginsa ta tanada, a cewar (Telegraph).

Shugaban kulob dinManchester United Ed Woodward ba zai bi kungiyar zuwa atisayen da take yi ba domin kammala cinikayyar wasu ‘yan wasa kafin a rufe kasuwar musayar ‘yan kwallo, in ji (ESPN).

Woodward na da kwarin gwiwar kammala cinikin dan wasan baya na Leicester Harry Maguire, da na matashin dan wasan tsakiya na Newcastle Sean Longstaff, in ji (London Evening Standard).

Nan da makonni biyu masu zuwa ne kocinArsenal Unai Emery zai yanke shawarar ko zai saki matashin dan wasan Ingila Reiss Nelson, zuwa Hertha Berlin a matsayin aro ko kuma a’a, a cewar (Sun).

Arsenal na kuma fatan ganin ta sayi Wilfred Zaha daga Crystal Palace kafin a rufe kasuwar musayar ‘yan kwallon.

Har yanzu kocinLiverpool Jurgen Klopp na son sayen dan wasa guda kafin a rufe ksuwa, amma ya bayyana cewa kulob ba zai kashe kudi kamar bara ba, inda suka kashe fam miliyan 170, in ji (Liverpool Echo)

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]