Kasuwar ƴan ƙwallo: Makomar Varane da Camara da Nagelsmann da Willock da Azpilicueta | BBC Hausa

h

Asalin hoton, Getty Images

Chelsea ta sha gaban Manchester United da Paris St-Germain a rige-rigen cimma yarjejeniya da dan wasan Real Madrid mai shekara 28, Raphael Varane. (Mundo Deportivo – in Spanish)

Mai tsaron bayan Guinea Ali Camara ɗan shekara 23, wanda ke taka leda a Young Boys na Switzerland, ya ja hankalin manyan ƙungiyoyin firimiya irinsu Liverpool, Arsenal, Crystal Palace, West Ham United da Norwich. (Team Talk)

Bayern Munich ta shiga tattaunawar dauko dan wasan RB Leipzig’s Julian Nagelsmann a matsayin sabon kocinta. (Independent)

Arsenal ta shiga tsaka mai wuya kan makomar ɗan wasan tsakiya Joe Willock mai shekara 21, wanda ke zaman aro a Newcastle, yayinda kulob din ke son sayar da ƴan wasan domin samun kudade. (Football London)

Kocin Atletico Madrid Diego Simone ya zaƙu ya cimma yarjejeniya da mai tsaron baya a Sifaniya Cesar Azpilicueta daga Chelsea. (El Gol Digital – in Spanish)

Manchester United da Liverpool na iya shiga zawarci a Torino’s kan dan wasan Italiya, Andrea Belotti, mai shekara 27, da ake alakantawa da AC Milan, Roma da Inter. Torino ta sanya ido kan mai buga gaba a Brazi,l Joao Pedro, mai shekara 29, a matsayin wanda zai maye gurbinsa. (Tuttosport)

Wolverhampton Wanderers ta kasance ƙungiya ta baya-bayanan da ake alakantawa da neman saye Tammy Abraham daga Chelsea. Hakazalika idon Aston Villad da West Ham da Leicester City na kan ɗan wasan. (Football Insider)

Tsohon kocin Tottenham Harry Redknapp na sa ran ɗan wasan Ingila, Harry Kane ya cigaba da zama a Spurs duk da rade-raden da ake na yiwuwar ya yi adabo da kungiyar a karshen kaka. (Goal)

Manchester City ta soma tattaunawa da Red Star Belgrade kan ɗan Serbiya Andrija Radulovic, mai shekara 18. (Sun)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...