Isra’ila ta ce an kashe ƴan ƙasarta sama da 600

A cewar gwamnatin ƙasar Isra’ila cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin Facebook sama da Isra’ilawa 600 ne aka kashe tun bayan harin da Falasɗinawa suka kaddamar a ranar Asabar.

Ta ƙara da cewa an yi garkuwa da mutum sama da 100, sannan 2,000 sun jikkata.

A Gaza, akalla mutum 313 ne aka kashe biyo bayan hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai, a cewar jami’an Falasɗinawa.

More from this stream

Recomended