INEC ta dakatar da Kwamishinanta na Adamawa

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dakatar da Kwamishinan Zabe na Adamawa Hudu Yunusa Ari.



Wannan matakin na zuwa ne bayan sanarwar da Kwamishinan ya yi a ranar Lahadin da ta gabata bayan zaben da aka gudanar a Adamawa.



Ari ya ayyana Aisha Dahiru Binani ta jam’iyyar All Progressives Congress, APC, a matsayin wadda ta lashe zaben duk da cewa jami’an tattara sakamakon zabe ne kadai aka ba su izinin yin hakan.



Wata wasika da ta fito 17 ga Afrilu, 2023, mai dauke da sa hannun Sakatariyar INEC, Rose Oriaran-Anthony, ta sanar da dakatar da Ari tare da umurtar Sakataren Gudanarwa na Adamawa ya maye gurbinsa.

More News

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...

Daurawa ya yi murabus daga muƙamin shugabancin Hisbah a Kano

Sheikh Aminu Daurawa ya yi murabus daga muƙaminsa na Shugaban Hisbah na Jihar Kano. Malamin yace ya yi iya kokarinsa wajen gyaran tarbiyar matasan Kano...