

An tura Abdulhamid Kabara a matsayin sabon kwamandan Hukumar Tsaro da Kare Dukiyar Kadarorin Gwamnatin da Fararen Hula (NSCDC) a Jihar Neja.
An tura Kabara ne bayan dakatar da Suberu Aniviye daga mukaminsa na kwamandan NSCDC a Neja haka ya biyo bayan mutuwar mutane 37 da ake zargi da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a hannun hukumar a Minna, babban birnin jihar, a ranar Alhamis.
Mai magana da yawun NSCDC a Neja, Abubakar Muti, a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar ya bayyana cewa Kabara ya karɓi ragamar shugabancin hukumar a ranar Juma’a, 18 ga Satumba.
Gwamnatin tarayya ta umarci a dakatar da Aniviye nan take bayan mutuwar mutanen 37 da ake tsare da su.
Sanarwar ta ce: “Fara aiki da sabon kwamandan ya yi ya zo ne a wani lokaci mai matuƙar muhimmanci ga hukumar, bayan mutuwar wasu da aka kama bisa zargin hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a jihar.”
Muti ya ce Kabara ya bayyana “jin zafi matuƙa kan rasa rayukan mutane” tare da mika ta’aziyya ga iyalan mamatan da kuma duk wanda abin ya shafa.
A cewar mai magana da yawun hukumar, Kabara ya jaddada cewa duk da NSCDC na da alhakin kama, bincike, aiwatar da doka da kuma yaƙi da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, “darajar rayuwar ɗan Adam dole ta kasance a gaba.”
Ya ce: “A irin wannan lokaci, bayan kamawa, bincike, aiwatar da doka da kuma yaƙi da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, dole mu tuna da gaskiya ɗaya: kowane rai yana da muhimmanci. Rashin rai na da zafi, kuma addu’o’inmu suna tare da iyalan da ke cikin jimami.”
Sabon kwamandan ya jaddada cewa aikin kare al’umma da aiwatar da doka dole ne ya tafi tare da kiyaye mutunci, tsaro da walwalar mutanen da ake tsare da su.