Hauhawar farashin kayan abinci ya zama bala’i ga ƴan Najeriya

Daga Dr. Marzuq Ungogo

A shekarar 2014, bayan na fara hidimar ƙasa an fara ban alawus ɗin likita, sai na je gida daga Gombe. Na yi wa ƙannena da iyaye ‘alheri’.

Ai kuwa mahaifina sai ya ƙi karbar kuɗin da na ba shi dubu goma ya ce sun yi yawa, kuma saboda me zan ɗorawa kaina ɗawainiya ko murmurewa ban yi ba. Mafaifiyata ta dage sai ya karɓa tun da ai ita ma ta amshi na ta.

Da a ka matsa, sai Baba ya karɓi kuɗi, ya ce to zai sayi buhun shinkafa (8,000) da katan ɗin taliya (2,000): duk wanda yaci a gidan sai na samu ƙarin lada.

Bayan ya yi haka, sai na ji daɗi sosai, sannan na yanke shawarar duk wata zan bada dubu goman a ci gaba da siya.

Har zuwa 2015 da na gama service farashin nan bai chanja da yawa ba, dubu goma za ta saya ma ka buhun shinkafa da katan ɗin taliya.

Sai dai kash, tun zuwan Mai Gaskiya lamari ya jagule! Jiya na ke ji wai buhun shinkafa ya kai 70,000. Hasbunallahu wa ni’imal wakeel! Ni kaɗai kawai sai tunane-tunane nake! Ko ya ya ma’aikatan albashi su ke yi? Oho! ‘Yan kasuwa dai da sun ji dugu-dugu sai su ƙara farashi tun daga kan mai yalo har mai kamfani. Amman albashi ya ƙi ya ƙaru dai-dai da ƙimar hauhawar farashi.

Duk duniya farashi da man dole ya na ƙaruwa duk shekara. Amman wannan lamarin na Najeriya ya wuce hankali! A cikin ƙasa da shekara goma, farashin abinci na neman ninkawa sau goma! Haba!

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...