Hajj 2021: Duk wanda ba a yi wa rigakafin korona ba ba zai yi ibadar ba – Saudiyya

Masu gudanar da aikin Hajji

Ma’aikatar Lafiya ta Saudiyya ta sharÉ—anta wa dukkan alhazai daga Ć™asashen waje su yi allurar rigakafin cutar korona sau biyu kafin gudanar da aikin Hajjin shekara ta 2021.

Jaridar Saudi Gazette ta ruwaito ma’aikatar na cewa wajibi ne a yi wa mahajjaci allura ta biyun, wadda Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta amince da ita. mako É—aya kafin ya isa Saudiyya,

Kazalika, alhazai za su je da takardar gwajin cutar wadda ke nuna cewa ba sa ɗauke da ita wadda kuma aka yi kwana uku kafin isarsu ƙasar.

Haka nan sai sun killace kansu na tsawon kwana uku. Alhazai za su fito ne kawai bayan gwaji ya tabbatar ba sa É—auke da cutar.

Ma’aiikatar ta kuma Ć™ayyade cewa ‘yan shekara 18 zuwa 60 ne kaÉ—ai za su yi aikin hajji na shekarar Hijira ta 1442.

Sauran sharuɗɗan sun haɗa da rataya alama a wuya da bayar da tazarar aƙalla mita ɗaya da rabi tsakanin alhazai. Sannan kuma rukunin mutum 100 ne za su riƙa gudanar da ayyukan ibada a lokaci guda.

Ga mazauna Saudiyya kuwa, ma’aikatar lafiyar Ć™asar ta ce tana sa ran yi wa kashi 60 cikin 100 na mazauna biranen Makka da Madina rigakafin korona kafin 1 ga watan Zul Hijja – watan aikin Hajji – a cewar rahoton Okaz.

Daga cikin Ć™a’idojin da aka shimfiÉ—a musu, wajibi ne duk ma’aikan Hajji sai sun yi rigakafin, wadda Ć™asar ta amince da ita, sau biyu.

Su ma alhazai mazauna Saudiyya dole ne a yi musu allurar sau biyu kafin 1 ga watan na Zul Hijjah.

Annobar korona ta sa Saudiyya ta hana alhazai daga ƙasashen waje shiga ƙasar domin gudanar da aikin Hajji na 2020, inda mutum kusan 1,000 ne kacal suka gudanar da ibadar.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...