Gwamnatin Najeriya Ta Kwaso ‘Yan kasarta 152 Da Suka Tsangare A Libya

Hukumar ba da agajin gaggawa ta kasa NEMA, ta karbi ‘yan Najeriya 152 da aka kwaso su daga kasar Libya.

Mutanen sun sauka ne a filin tashin jirage na Murtala Muhammad da ke birnin Legas a cewar Shugaban hukumar a shiyyar kudu maso yammacin Najeriya, Ibrahim Farinloye kamar yadda ya fada a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.

Bayanai sun yi nuni da cewa ‘yan Najeriyar na daga cikin wadanda suka makale a kasar ta Libya wadanda suka je kasar a kokarinsu na ketara tekun Meditareniya don kai wa ga kasashen Turai.

Hukumar ta NEMA ta ce mutanen da aka kwaso tare da hadin gwiwar hukumar da ke kula da masu yin kaura ta kasa da kasa, sun hada da manyan mata 54, manyan maza da yara kanana 73.

Daruruwan dubban mutane ne ake yaudara zuwa kasar Libya da niyyar bi ta tekun Meditareniya mai cike hadari don a tsallaka da su zuwa kasashen turai.

Bakin hauren kan bi ta kwale-kwale marasa inganci wajen yin tafiyar a teku, abin da kan kai ga mutuwar daruruwan mutane.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...