Gwamnatin Kano tana yin kafar ungulu ga shirin miƙa mulki—NNPP

Jam’iyyar mai jiran gado a Jihar Kano, wato NNPP, ta yi zargin gwamnatin jihar mai barin gado da yin kafar ungulu ga shirin miƙa mulki a ranar 29 ga watan Mayu na wannan shekarar.

A wani taron manema labarai a ranar Juma’a, shugaban kwamitin miƙa mulki na gwamna a jam’iyyar NNPP Dr Abdullahi Baffa Bichi ya yi zargin cewa gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, da gangan tana kawo cikan ga shirin miƙa mulki.

Ya ce gwamnatin ta bai wa jam’iyyar NNPP gurbi uku kawai a cikin kwamitin da aka kafa don miƙa mulki hannun sabuwar gwamnati.

Sai dai gwamnati mai barin gado ta Dr. Abdullahi Umar Ganduje ta musanta wannan zargi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]