Gwamnati ta fadi dalilin da ya sa aka shiga matsalar lantarki

Gwamnatin ta ce an samu matsala ne a babban layin samar da lantarki na ƙasa.

Wata sanarwar daga ofishin ministan lantarki na Najeriya Injiniya Abubakar Aliyu ta ce ana gudanar da bincike domin gaggauta magance matslar.

An fuskanci katsewar lantarki a sassan Najeriya a ranar Juma’a.

Sanarwar ta ce: “muna sanar da al’umma cewa matsalar ta faru ne karfe 18:30 a ranar 8 ga Afrilu, wanda ya haifar da matsalar lantarki a sassa da dama na ƙasa.”


More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]